DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC ta musanta ba ‘yan majalisar dokokin Nijeriya tikitin takara na yin tazarce babu hamayya a 2027

-

Jam’iyyar APC ta musanta rahotannin da ke yawo a kafafen yada labarai da ke cewa ta bai wa dukkanin ’yan majalisar tarayya da ke kan kujeru tikitin tsayawa takara don tazarce ba tare da hamayya ba, tana bayyana irin wannan labari a matsayin “marar tushe bare makama.”

A wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar na kasa, Felix Morka, ya fitar, jam’iyyar APC ta bukaci ’ya’yanta da al’umma gaba daya da su yi watsi da abin da ta kira “rahoton karya da ake ikirarin ya fito daga jam’iyyar.”

Google search engine

Wannan bayani ya fito ne a daidai lokacin da ake kara yada jita-jita game da tsarin zaben fitar da ’yan takarar jam’iyyar gabanin zabe mai zuwa.

Morka ya jaddada cewa duka hukuncin da jam’iyyar za ta yanke za a sanar da su ne ta hanyoyi na hukuma da aka tabbatar da sahihancinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsare-tsaren Tinubu na farfaɗo da martabar Nijeriya a duniya -Kashim Shatima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na sake gina martabar Nijeriya a idon duniya tare...

Gwamnatin Nijeriya na shirin dakatar da shigo da kayan tsaro daga waje

Gwamnatin Nijeriya ta yi niyyar kera dukkan makami da ake buƙata a cikin gida nan da shekara biyu zuwa biyar masu zuwa. Minista a ma'aikatar Tsaron...

Mafi Shahara