DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Fursunoni 200 sun arce daga gidan yarin kasar Pakistan

-

Jami’ai a kasar Pakistan sun bayar da rahoton cewa fiye da fursunoni 200 sun tsere daga gidan yari a birnin Karachi bayan da aka bar su su fita daga dakunansu sakamakon girgizar kasa da aka ji sau da dama a yankin.

Zia-ul-Hasan Lanjar, kwamishinan shari’a na jihar, ya shaida wa ’yan jarida a wurin cewa an bai wa daruruwan fursunoni damar fita zuwa harabar gidan yari saboda girgizar kasar.

Google search engine

Farkon tserewar fursunonin ya faru ne da daren Litinin kafin karfe 12 na dare, kuma ya ci gaba har zuwa wayewar garin Talata, in ji kwamishinan.

’Yan sanda sun ce fursunonin sun kwace bindigu daga hannun ma’aikatan gidan yari, abin da ya janyo musayar wuta, kafin daga bisani su tilasta a bude kofar shiga ta gaba.

A ranar Talata, wani wakilin kamfanin Reuters da ke wurin ya ga tagogi fasassu da kuma na’urorin lantarki da suka lalace a cikin gidan yari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

George Akume Har Yanzu Shi Ne Sakataren Gwamnatin Tarayya – Fadar Shugaban Kasa

Fadar Shugaban Nijeriya ta musanta jita-jitar da ke yawo cewa an sauke Sanata George Akume daga matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF). A wata sanarwa da mai...

Yawaita buga sabbin takardun kudi da da aka rika yi a gwamnatin Buhari ne ya gurgunta darajar Naira – Oshiomhole

Sanata Adams Oshiomhole, ya zargi tsohuwar gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari da taka raws wajen gurgunta tattalin arziki Nijeriya Ya bayyana hakan a wani taro...

Mafi Shahara