Jami’an rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi sun samu nasarar dakile wani yunkurin kai hari da matasa suka shirya yi wa wani mutum mai shekaru 37 da haihuwa da ake zargi da cin zarafin diyar matarsa wato ‘agolarsa’ mai shekaru 15.
A cewar rundunar, jami’an da ke karkashin shirin “Operation Restore Peace” wanda CSP Kim Abert ke jagoranta, sun samu bayanan sirri masu inganci wanda ya ba su damar dakile harin da ake shirin kai wa mutumin mai suna Wisdom Benoie.
Kakakin rundunar, SP Ahmed Wakil, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a Bauchi.
Sanarwar ‘yan sandan ta ce binciken farko-farko sun bayyana cewa mutumin na auren mahaifiyar budurwar ne. Wanda ake zargin ya amsa laifinsa.