Jam’iyyar APC mai mulkin Nijeriya ta soki kalaman tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar, da tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, da kuma tsohon gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, da suka yi cewa shugaba Bola Tinubu na amfani da talauci a matsayin makamin wajen hana ‘yan Nijeriya su juya masa baya.
Jiga-jigan siyasar uku sun yi wannan ikirarin ne a karshen mako wajen taron da aka gudanar a Abuja don murnar cika shekaru 60 na Rotimi Amaechi.
A wata sanarwa da ya fitar, kakakin jam’iyyar APC, Felix Morka, ya caccaki ‘yan siyasar uku, inda ya ce sun kasa kawar da talauci a jihohinsu ko kasar duk da cewa sun rike kujerun gwamnati a lokaci daban-daban