DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP a Jihar Kaduna ta kalubalanci gwamnatin Jihar saboda sabbin hare-haren ‘yan bindiga a jihar

-

Jam’iyyar PDP a Jihar Kaduna ta yi tir da sabbin hare-haren ‘yan bindiga a jihar inda ta bayyana hakan a matsayin abin takaici da kuma gazawar gwamnati.

PDP ta ce, harin da aka kai a kauyukan Kagara da Ugom da ke kananan hukumomin Giwa da Kajuru sun yi sanadiyar rasa rayukan mutane 2 da jikkata wasu tsakanin 4 zuwa 6 ga watan Yuni,2025.

Google search engine

A bayanin da jam’iyyar ta fitar a ranar Asabar wanda ke dauke da sa hannun Shugaban jam’iyyar na Jihar Kaduna, Edward Masha ya nuna bakin cikinsu na rasa rayukan da halin da iyalan mamatan za su shiga.

Jam’iyyar ta yi kira ga gwamnatin Uba Sani da su gaggauta bitar tsarin tsaron jihar musamman ma’aikatar tsaro da harkokin cikin gida na jihar da su falka daga bacci don sauke nauyin da ke a wuyansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara