Hukumar yaki da safarar mutane ta Nijeriya NAPTIP, haɗin guiwa da hukumar tsaro ta DIA, sun kubutar da mutane 20 daga gungun masu safarar mutane da ke aiki a ƙasashen Equatorial Guinea da Togo da kuma Najeriya.
Jami’an NAPTIP sun bayyana cewa waɗanda aka ceto an yaudare su da alkawarin samar musu ayyuka masu albashi mai tsoka, sai dai daga bisani aka tilasta musu yin aikin karfi.
Jami’in hulɗa da jama’a na NAPTIP, Vincent Adekoye, ya ce an kama wasu mutane uku da ake zargi da hannu a safarar a Abuja, Osun da Nasarawa, yayin da hukumar ta ƙara sa ido a kan iyakokin ƙasa don hana safarar mutane.