Saboda yawaitar matsalar rashin tsaro, Gwamnatin Jihar Nasarawa ta bayyana shirinta na kafa sansanonin tsaro a kowane daga cikin yankunan sanatoci guda uku na jihar, domin kara inganta zaman lafiya da tsaro.
Daily Nigerian ta ruwaito kwamishinar kudi da tsare-tsare ta jihar, Munira Abdullahi, na bayyana haka yayin taron jin ra’ayin jama’a kan kasafin kudin yankin Nasarawa ta Arewa da aka gudanar a karamar hukumar Keffi, ranar Laraba.
Munira, wadda Babban Sakataren ma’aikatar kudi, Polinus Wahe, ya wakilta, ta ce matakin ya biyo bayan korafin jama’a kan bukatar karin tsaro a yankunansu.
Gwamnatin ta ce wannan shiri na daga cikin dabarun da take dauka domin tinkarar kalubalen tsaro a jihar.