DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin nasarawa za ta gina sansanonin tsaro a kowane yankin Sanata na Jihar

-

Saboda yawaitar matsalar rashin tsaro, Gwamnatin Jihar Nasarawa ta bayyana shirinta na kafa sansanonin tsaro a kowane daga cikin yankunan sanatoci guda uku na jihar, domin kara inganta zaman lafiya da tsaro.

Daily Nigerian ta ruwaito kwamishinar kudi da tsare-tsare ta jihar, Munira Abdullahi, na bayyana haka yayin taron jin ra’ayin jama’a kan kasafin kudin yankin Nasarawa ta Arewa da aka gudanar a karamar hukumar Keffi, ranar Laraba.

Google search engine

Munira, wadda Babban Sakataren ma’aikatar kudi, Polinus Wahe, ya wakilta, ta ce matakin ya biyo bayan korafin jama’a kan bukatar karin tsaro a yankunansu.

Gwamnatin ta ce wannan shiri na daga cikin dabarun da take dauka domin tinkarar kalubalen tsaro a jihar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam'iyyar na kasa Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan...

Mafi Shahara