DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar wakilan Nijeriya ta kwato harajin Naira bilyan 86.5 da ba a saka asusun gwamnati ba

-

Kwamitin majalisar wakilai mai kula da harkokin dukiyar al’umma ya gargadi kamfanonin hakar mai 13 da su bayyana a gabansa domin amsa tambayoyi kan binciken da ake yi na rashin saka makudan kudaden haraji a asusun gwamnatin tarayya ko kuma su fuskanci takunkumi.

Kwamitin na zargin gwamnati na bin kamfanonin bashin kimanin dala miliyan 456.95 wanda ya kai Naira biliyan 731.12, na kudaden shiga da ba su saka wa gwamnati ba.

Google search engine

A cikin wata sanarwa da kakakin majalisar wakilan Nijeriya Mista Akin Rotimi ya fitar, majalisar ta ce duk da gayyatar kamfanonin da kuma sanarwar da aka buga a jaridun kasar, kamfanonin sun ki bayyana a gaban kwamitin.

Sanarwar ta kuma ruwaito shugaban kwamitin, Bamidele Salam yana cewa, duk kamfanin da ya kasa bayyana zai fuskanci fushin doka.

Gargadin na zuwa ne a daidai lokacin da kwamitin ya sanar da kwato karin Dala milyan 15.7, kimanin Naira bilyan 25 daga wasu kamfanonin mai, wanda ya sa adadin kudaden da aka kwato ya kai Naira bilyan 86.5.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam'iyyar na kasa Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan...

Mafi Shahara