Shugaba Bola Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta tabbatar da cewa kowane dan Najeriya ya ji tasirin shugabanci a karkashin gwamnatinsa.
Ya bayar da wannan tabbacin ne a wajen kaddamar da wasu hanyoyi a birnin tarayya Abuja da Wike ya yi.
Shugaban wanda mataimakin kakakin majalisar, Benjamin Kalu ya wakilta ya ce gwamnatinsu za ta ci gaba da yin aiki tukuru domin samar da ayyukan more rayuwa da za su inganta rayuwar ‘yan kasa.