Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana aniyarsa ta ƙara albashi ga Ƙungiyar mawakan Gwamnati da ke aiki da shi, bayan sun rera waka cikin yaren kasar Sin.
Wike ya bayyana hakan ne a ranar Alhamis Yayin kaddamar da sabuwar hanyar da aka kamala daga Mabushi zuwa Judges’ Quarters a Katampe, Abuja.
A Yayin taron, shugaban Ƙungiyar mawakan ya rera wata waka cikin salon yaren Sin, lamarin da ya jawo dariya da farin ciki a wajen mahalarta, ciki har da Minista Wike da ya nuna gamsuwarsa da salon mawakan.