DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai manyan ‘yan siyasa daga Kudancin Nijeriya da ke cikin hadakar siyasa da Atiku – Hakeem Baba-Ahmed

-

Tsohon mai bai wa shugaban kasa Bola Tinubu shawara kan harkokin siyasa, Hakeem Baba-Ahmed, ya musanta ikirarin da ake yi na cewa ‘yan siyasar Arewa ne ke jagorantar kawancen da ke adawa da gwamnatin Tinubu.

Da ya ke magana a gidan talabijin na Arise a Litinin dinnan Hakeem Baba-Ahmed, wanda a kwanakin baya ya yi murabus daga mukaminsa, ya bayyana cewa kawancen da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ke jagoranta, ba shiri ne na yankin Arewa kaɗai ba.

Google search engine

Ya ce hadakar ‘yan siyasa ba sabon abu bane a Nijeriya, inda ya ce duk hadakar da ta faru a kasar ta shafi ‘yan kuduncin ƙasar.

A cewar sa akwai ‘yan Kudu da ke cikin wannan magana ta hadaka dumu-dumu, ciki harda, Rotimi Amaechi, tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, sa’annan akwai mutane da yawa daga Kudancin Nijeriya da ke kan harkar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Mafi Shahara