Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya za ta hada kai da abokan huldarta na kasa da kasa domin bai wa matasan kasar kwarin gwiwar sana’o’ar noma na zamani domin dogaro da kai da kuma inganta samar da abinci.
Tinubu ya bayyana haka ne a ranar Litinin,yayin kaddamar da kayan aikin noma a Abuja, inda ya kuma kaddamar da manyan motocin noma 2,000 da na’urori na musamman na gonaki sama da 9,000.
Ya ce sauye-sauyen da gwamnatinsa ta bullo da shi na da nufin ganin noma ya zama abin burgewa ga matasan Nijeriya.