Kungiyar Sanatocin Arewa ta yi Allah-wadai da ajalin matafiya 12 ‘yan jihar Kaduna da wasu suka yi a jihar Filato yayin da suke tafiya daurin aure a karamar hukumar Pan da ke jihar.
A cikin wata sanarwa da ya fitar Litinin dinnan, Shugaban kungiyar Sanata Abdulaziz Musa Yar’Adua, ya bayyana harin a matsayin rashin rashin imani, yana mai jaddada cewa irin wannan mummunan tashe-tashen hankula na bukatar gaggauta yin abinda ya dace a kansu.
Ya jaddada cewa irin wannan kisa na rashin hankali da ake yi wa ‘yan kasa wayanda ba su ji ba ba su gani ba, abu ne da ba za a amince da shi ba, don haka akwai bukatar a dauki matakin gaggauwa dan kaucewa ci gaba da faruwar hakan.