DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan gudun hijira a jihar Binuwai sunyi zanga-zangar nuna rashin amincewarsu da mummunan yanayi da suka shiga a sansaninsu

-

Rahotanni sun nuna cewa ‘yan gudun hijira daga al’ummar Yelwata da ke karamar hukumar Guma a jihar Binuwai sun nuna rashin amincewarsu da halin da suke ciki a sansanin da gwamnatin jihar ta samar.

Mutanen da suka rasa matsugunansu sun yi sansani ne a Kasuwar Duniya da ke Makurdi, biyo bayan hare-haren da wasu masu dauke da makamai suka kai wa al’umma, lamarin da ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama tare da kone gidaje.

Google search engine

Shugaban kasa, Bola Tinubu da gwamnonin jihohin Arewa ta tsakiya, sun ziyarci jihar Binuwai a ranar Laraba, domin ganawa da masu ruwa da tsaki kan yadda za a kawo karshen tashe-tashen hankula a jihar.

Shugaban ya kuma ziyarci asibitin da wasu daga cikin wadanda harin ya rutsa da su ke karbar kulawa.

Masu zanga-zangar sun fita kan titunan Makurdi tare da toshe duk wasu manyan hanyoyin shiga sansanin na wucin gadi da ke kan titin George Akume a birnin Makurdi, domin nuna rashin ɓacin ransu kan cin zarafi da suke zargin an yi musu tun lokacin da suka isa sansanin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon Gwamnan jihar Kwara Cornelius Adebayo ya rasu yana da shekaru 84

Tsohon Gwamnan jihar Kwara kuma Ministan Sadarwa na baya, Cornelius Adebayo, ya rasu yana da shekara 84 a Abuja da safiyar Laraba nan. Dansa na fari,...

An karrama ma’aikacin gwamnatin Jigawa a Saudiyya bisa dawo da kuɗin da ya tsinta

Wani ma’aikacin gudanarwa a Saudiyya, Muhammed Salalah, ya mika kwafin Alkur’ani Mai Tsarki ga Daraktan Rediyon Jigawa, Malam Isma’il Babura, a matsayin kyauta mai daraja...

Mafi Shahara