Jami’an hukumar EFCC mai yaki da yi wa tattalin arzikin Nijeriya tu’annati, sun kama tsohon babban jami’in kudi na kamfanin NNPCL Umar Isa, bisa zarginsa da almundahanar kudin da suka kai dala biliyan 7.2 na gyaran matatun mai na Kaduna, Warri da Fatakwal.
Haka kuma EFCC ta kama Jimoh Olasunkanmi, tsohon manajan darakta na matatar mai na Warri, da manajan daraktan matatar na yanzu, Tunde Bakare da kuma tsofaffin manajan daraktocin matatar man Fatakwal, Ahmed Dikko Ibrahim Onoja, kamar yadda wata majiya ta shaida wa gidan Talabijin na Channels.
Sai dai duk kokarin jin ta bakin Kakakin EFCC, Dele Oyewale, hakan ya ci tura.