DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

-

By Salisu Ado Sulaiman

Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba.

Google search engine

Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar Kingsley Uwa wanda ya jagoranci sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya tsakanin bangarorin biyu a karamar hukumar Gassol da ke jihar, ya nuna illolin da ke tattare da daukar doka a hannu ga jama’a.

Masu ruwa da tsaki da suka hadar da sarakunan gargajiya da sauran jagororin al’umma, sun halarci zaman sulhu da ya gudana a shalkwatar rundunar da ke Jalingo babban birnin jihar.

Wata sanarwa da sashen yada labarai na rundunar ya fitar, ta bayyana cewa akwai bukatar samun hadin kai daga dukkanin bangarori don ganin bayan matsalolin tsaro da ke addabar al’umma.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Shugaban kasar Uganda mai shekaru 80, zai sake tsayawa takara bayan shafe shekara 39 kan mulki

Jam'iyyar NRM mai mulki a kasar Uganda ta ce shugaban kasar Yoweri Museveni zai sake neman tsayawa takara a zaben da za a gudanar a...

Mafi Shahara