Gwamnatin jihar Kaduna ta yi watsi da ikirarin da wani tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai ya yi na cewa dukkanin ayyukan da shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar a jihar kwanan nan an fara su ne a gwamnatinsa.
El-Rufai, wanda ya mulki Kaduna daga 2015 zuwa 2023, a wata hira da manema labarai a ranar Litinin ya bayyana cewa ayyukan da shugaba Tinubu ya kaddamar a ranar Alhamis din da ta gabata, aikinsa ne
Sai dai kuma a wani martani da ya mayar, babban sakataren yada labarai na gwamna Uba Sani, Ibraheem Musa ya bayyana ikirarin tsohon gwamnan a matsayin karya ce tsantsa da kuma yunkurin canza tunanin mutane.
A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya bayyana cewa ayyukan da ake magana a kai an fara su ne kuma an kammala su a karkashin gwamnati mai ci.