DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kaduna ta yi watsi da ikiranin da El-Rufai ya yi kan ayyukan da Tinubu ya kaddamar cewa shi ne ya fara su

-

Gwamnatin jihar Kaduna ta yi watsi da ikirarin da wani tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai ya yi na cewa dukkanin ayyukan da shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar a jihar kwanan nan an fara su ne a gwamnatinsa.

El-Rufai, wanda ya mulki Kaduna daga 2015 zuwa 2023, a wata hira da manema labarai a ranar Litinin ya bayyana cewa ayyukan da shugaba Tinubu ya kaddamar a ranar Alhamis din da ta gabata, aikinsa ne

Google search engine

Sai dai kuma a wani martani da ya mayar, babban sakataren yada labarai na gwamna Uba Sani, Ibraheem Musa ya bayyana ikirarin tsohon gwamnan a matsayin karya ce tsantsa da kuma yunkurin canza tunanin mutane.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya bayyana cewa ayyukan da ake magana a kai an fara su ne kuma an kammala su a karkashin gwamnati mai ci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jami’ar gwamnatin tarayya da ke Dutse a jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 bisa zarginsu da satar jarrabawa

Jami'ar tarayya da ke jihar Jigawa ta kori dalibai 20 tare da dakatar da wasu 15 daga karatu bisa samunsu da laifin satar jarabawa. Rahotanni sun...

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Mafi Shahara