DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kaduna ta yi watsi da ikiranin da El-Rufai ya yi kan ayyukan da Tinubu ya kaddamar cewa shi ne ya fara su

-

Gwamnatin jihar Kaduna ta yi watsi da ikirarin da wani tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai ya yi na cewa dukkanin ayyukan da shugaban kasa Bola Tinubu ya kaddamar a jihar kwanan nan an fara su ne a gwamnatinsa.

El-Rufai, wanda ya mulki Kaduna daga 2015 zuwa 2023, a wata hira da manema labarai a ranar Litinin ya bayyana cewa ayyukan da shugaba Tinubu ya kaddamar a ranar Alhamis din da ta gabata, aikinsa ne

Google search engine

Sai dai kuma a wani martani da ya mayar, babban sakataren yada labarai na gwamna Uba Sani, Ibraheem Musa ya bayyana ikirarin tsohon gwamnan a matsayin karya ce tsantsa da kuma yunkurin canza tunanin mutane.

A wata sanarwa da ya fitar ranar Talata, ya bayyana cewa ayyukan da ake magana a kai an fara su ne kuma an kammala su a karkashin gwamnati mai ci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo ya tsawaita kwantiraginsa da kungiyarsa ta Al Nassr har zuwa shekarar 2027

Cristiano Ronaldo ya tsawaita kwantiraginsa da kungiyar Al Nassr ta kasar Saudiyya a hukumance, inda zai ci gaba da zama a birnin Riyardh na kasar...

Mataimakin shugaban Nijeriya Kasshim Shettima ya tafi kasar Ethiopia

A safiyar ranar Alhamis Kasshim Shettima ya tashi daga Abuja zuwa birnin Adis Ababa domin ziyarar aiki bisa gayyatar da Firaministan kasar Dr Abiy Ahmed...

Mafi Shahara