DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu zai ba da tallafin karatu a Nijeriya ga daliban yankin Karebiyan

-

Shugaban kasa Bola Tinubu ya amince da bayar da tallafin karatu ga daliban kungiyar kasashen gabashin Karebiyan OECS don yin karatu a jami’o’in Najeriya, daga shekara mai zuwa.

A yayin wani taron manema labarai na hadin gwiwa a Gros Islet a ranar Litinin tare da Firayim Ministan Saint Lucian Philip J. Pierre, Shugaba Tinubu ya ce tuni aka fara shirin kuma za a aiwatar da shi a karkashin wani kwamitin hadin gwiwa tsakanin Najeriya da kasashe mambobin kungiyar OECS.

Ya kuma tabbatar da cewa suna ci gaba da tattaunawa kan bai wa jami’an diflomasiyya daga kasashen OECS izinin shiga Nijeriya ba tare da biza ba.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

’Yan majalisar wakilai bakwai daga Akwa Ibom sun sauya sheka zuwa APC

Ana cigaba da samun rahotannin sauyin sheka a majalisar wakilai, yayin da ’yan majalisa bakwai daga Jihar Akwa Ibom suka koma jam’iyyar APC. Wadanda suka...

Jam’iyyar Labour tsagin Julius Abure ta ba Peter Obi sa’o’i 48 ya fice daga jam’iyyar saboda shiga hadakar ADC

Jam’iyyar Labour karkashin jagorancin Julius Abure ta bai wa tsohon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi, wa’adin sa’o’i 48 da ya fice daga jam’iyyar, bisa...

Mafi Shahara