DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya na cikin barazana muddin ba’a sauya kundin tsarin mulki ba – tsohon gwamnan Akwa Ibom

-

Tsohon gwamnan Akwa Ibom, Victor Attah, ya yi kira da a samar da sabon kundin tsarin mulki kafin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sauka daga mulki, yana mai gargadin cewa Najeriya za ta kara fadawa cikin matsaloli idan hakan bai faru ba.

Attah wanda jaridar Punch ta ambato na bayyana kundin tsarin mulkin 1999 a matsayin mai cike da kura-kurai da rashin dacewa da yanayin Najeriya.

Google search engine

Ya ce Tinubu shi ya fi dacewa da jagorantar sauyin, duba da irin kalubalen da ya fuskanta a matsayin gwamnan Legas game da tsarin mulkin yanzu.

A karshe, Attah ya bukaci a gina sabon tsarin da zai karfafa hadin kai, adalci da ci gaban kasa, yana mai cewa lokaci ya yi da Najeriya za ta dauki wannan matsaya da aka dade ana son cimma wa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnan Bauchi ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar

Gwamnan Bauchi Bala Muhammad ya sanya hannu kan dokar kirkirar sabbin masarautu 13 a fadin jihar. Daily Trust ta ruwaito cewa a lokacin da yake sanya...

Kenya da Senegal sun kulla yarjejeniyar shige da fice ba tare da biza ba

Gwamnatocin Kenya da Senegal sun bai wa juna damar shige da fice ga 'yan kasashensu ba tare da biza ba na tsawon kwanaki 90. DW Africa...

Mafi Shahara