DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar zaben Nijeriya INEC ta karɓi ƙarin takardu 12 da ke neman rijistar sabbin jam’iyyu

-

Hukumar zaben Nijeriya INEC ta bayyana cewa ta karɓi ƙarin buƙatun rajista guda 12 daga ƙungiyoyin da ke neman zama jam’iyyun siyasa a kasar, inda hakan ya kai yawan waɗanda ke neman rajistar zuwa 122.

INEC ta bayyana hakan ne cikin wata sanarwa da Kwamishinan Ƙasa mai kula da Yada Labarai da Ilimin Zaɓe, Mista Sam Olumekun, ya fitar a ranar Alhamis.

Google search engine

Sanarwar ta jaddada cewa ana aiwatar da tantance waɗannan buƙatu cikin gaskiya da adalci, kuma hukumar za ta rika sanar da ‘yan ƙasa ci gaban da ake samu.

Jaridar The Nation ta ce hukumar ta kuma ja hankalin ƙungiyoyin da ke neman rajista da su kasance da daidaito wajen bayyana shugabanninsu don guje wa tsaiko a cikin aikin tantancewa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara