DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Babu maganar cewa zan yi wa Atiku mataimaki, takarar shugaban kasa zan yi a 2027 – Peter Obi

-

Peter Obi da ya yi wa jam’iyyar LP takarar shugaban kasa a zaben 2023 ya bayyana cewa zai sake tsayawa takarar kujerar Shugaban Ƙasa a shekarar 2027.

Tsohon Gwamnan jihar Anambra ya kuma yi watsi da jita-jitar cewa zai tsaya takarar mataimakin Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP a yayin zaben.

Google search engine

A cikin shirin Sunday Politics na gidan talabijin na Channels Peter Obi ya zai tsaya takarar ne don ya cancanta.

Da aka tambaye shi ko yana shirin zama mataimakin Atiku a zaɓen 2027, Obi ya ce, “wannan maganar babu ita; babu wanda ya taɓa tattaunawa da ni a kai. Mutane na ɗaukar abubuwa da yawa da kansu. Babu wanda ya taɓa zama da ni.

Tsohon gwamnan jihar Anambra ya jaddada cewa har yanzu mamba ne mai ƙwazo a jam’iyyar Labour Party, kodayake yana cikin gamayyar jam’iyyun adawa ƙarƙashin African Democratic Congress (ADC), da aka kafa don ƙwace mulki daga hannun Shugaba Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), wanda ke neman wa’adin mulki na biyu a shekarar 2027.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara