DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’an tsaron Nijar sun hallaka ‘yan ta’adda kusan 200 a jihar Tillaberi

-

Rundunar tsaron sama ta Nijar ta yi ruwan wuta ga wani gungun ‘yan ta’adda a lokacin da suke wani taron tattauna shirin yiwuwar kai wani sabon hari kan sansanin sojin kasar da misalin karfe 6 na safiyar Lahadin nan kamar yadda rundunar sojin kasar ta ruwaito a shafinta na facebook.

Kazalika rundunar ta ce a yayin wannan barin wuta ta kona babura da motoci tare da lalata wadansu kayayyakin ‘yan ta’addar da dama.

Google search engine

Wannan nasara dai na zuwa ne bayan wadansu tagwayen hare-hare da ‘yan ta’addar suka kai a ranar Juma’ar da ta gabata a garuruwan Bouloundjounga da Samira cikin karamar hukumar Gotey da ke jihar Tillaberi inda nan ma jami’an tsaron suka yi nasarar hallaka wadansu mahara 41 tare da kwace tarin makaman yaki da babura yayin da sojojin kasar 10 suka kwanta dama, wadansu 15 suka jikkata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara