DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’an tsaron Nijar sun hallaka ‘yan ta’adda kusan 200 a jihar Tillaberi

-

Rundunar tsaron sama ta Nijar ta yi ruwan wuta ga wani gungun ‘yan ta’adda a lokacin da suke wani taron tattauna shirin yiwuwar kai wani sabon hari kan sansanin sojin kasar da misalin karfe 6 na safiyar Lahadin nan kamar yadda rundunar sojin kasar ta ruwaito a shafinta na facebook.

Kazalika rundunar ta ce a yayin wannan barin wuta ta kona babura da motoci tare da lalata wadansu kayayyakin ‘yan ta’addar da dama.

Google search engine

Wannan nasara dai na zuwa ne bayan wadansu tagwayen hare-hare da ‘yan ta’addar suka kai a ranar Juma’ar da ta gabata a garuruwan Bouloundjounga da Samira cikin karamar hukumar Gotey da ke jihar Tillaberi inda nan ma jami’an tsaron suka yi nasarar hallaka wadansu mahara 41 tare da kwace tarin makaman yaki da babura yayin da sojojin kasar 10 suka kwanta dama, wadansu 15 suka jikkata.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Daga 2026 ₦500,000 kawai ɗan Nijeriya zai iya cira a banki cikin sati ɗaya – CBN

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya sake fasalin dokokin cire kuɗi daga bankuna kan sabon tsarin da zai fara aiki daga watan Janairun 2026. Babban bankin ya...

Ƴan kwangila sun girke akwatin gawa a ofishin ma’aikatar kuɗin Nijeriya

‘Yan kwangila sun girke akwatin gawa a kofar shiga ofishin ma’aikatar kudin Nijeriya da ke Abuja.   ‘Yan kwangilar, karkashin inuwar kungiyarsu ta 'yan asalin Nijeriya sun...

Mafi Shahara