DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya umarci a sauke tutar Nijeriya zuwa rabin sanda a fadin kasar domin jimamin rasuwar Buhari

-

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da rasuwar tsohon shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu yau Lahadi a birnin London da misalin ƙarfe 4:30 na yamma bayan doguwar jinya.

Shugaba Tinubu ya sha mika ta’aziyyarsa ga uwargidan marigayin, Hajiya Aisha Buhari, tare da umartar mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, da ya tafi Birtaniya domin dawo da gawar shugaban zuwa gida Najeriya.

Google search engine

Buhari ya shugabanci Najeriya a matsayin shugaban ƙasa na mulkin farar hula daga 2015 zuwa 2023, kuma ya rike kujerar shugaban ƙasa a lokacin mulkin soja daga shekarar 1984 zuwa 1985.

A wani mataki na girmamawa, Shugaba Tinubu ya umarci a sauke tutar Najeriya zuwa rabin sanda a fadin kasar, a matsayin alamar alhini da karramawa ga rayuwar marigayin shugaban ƙasa.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An dage jana’izar marigayi Muhammad Buhari zuwa ranar Talata -Dikko Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, ya sanar da shirye-shiryen jana'izar tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi, 13 ga Yuli,...

Jam’iyyar ADC ta sanar da kwana uku na alhinin rashin tsohon Shugaban Nijeriya, Muhammadu Buhari

Jam’iyyar ADC ta bayyana kwanaki uku na zaman makoki ga mambobinta don girmama marigayi tsohon shugaban ƙasa Muhammadu Buhari, wanda ya rasu a ranar Lahadi...

Mafi Shahara