DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

-

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama’a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba.

Rahotanni sun bayyana cewa Ibikunle ya kai wata daliba, Miss Glory Ojochegbe Samuel (24GE1034), ɗaliba a sashen da yake koyarwa, zuwa wani otal a Anyigba, inda aka ce ya rasu yana tare da ita.

Google search engine

Bayan haka, dalibar ta sanar da ma’aikacin otal ɗin wanda suka garzaya da mamacin zuwa asibiti, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

Kakakin rundunar ‘yan sanda ta jihar, William Aya, ya ce an tsare dalibar a hedikwatar ‘yan sanda da ke Lokoja domin gudanar da bincike na musamman a sashen binciken manyan laifuka na rundunar.

A nata bangaren, jami’ar Prince Abubakar Audu ta bayyana bakin cikinta kan lamarin, tana mai cewa wannan al’amari ne mai matuƙar tayar da hankali da kuma buƙatar cikakken bincike.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Majalisar dattawan Nijeriya ta ba shugaban NNPCL wa’adin mako 3 kan batan Naira tiriliyan 210

Majalisar dattawan Najeriya ta bai wa Shugaban kamfanin man fetur na kasa (NNPCL), Bayo Ojulari, wa’adin makonni uku domin ya bayyana cikakken bayani kan inda...

Mafi Shahara