DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Adadin kujerun APC ya kai 72 a majalisar Dattawa, daga guda 50 da take da su a 2023

-

Majalisar dattawa a Najeriya ta karɓi Sanatoci hudu daga jam’iyyar PDP da suka sauya sheka zuwa APC, lamarin da ya ƙara karfafa rinjayen APC a zauren majalisar.

Sanatocin da suka sauya sheka su ne: Sanata Ekong Samson daga Akwa Ibom South, da Sanata Etim Bassey Akwa Ibom North East, sai Sanata Francis Fadahunsi Osun East, da Sanata Olubiyi Fadeyi Osun Central.

Google search engine

Gidan talabijin na Channel ya tattaro cewa, bayan sauya shekar, APC yanzu tana da kujeru 72 a Majalisar Dattawa ta 10, daga 50 da ta fara da su a watan Yunin shekarar 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara