DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ƙungiyar Super Falcons ta Najeriya za ta buga wasan ƙarshe a gasar kofin mata na Afirka

-

Ƙungiyar Super Falcons ta Najeriya za ta kara da ƙasar Maroko a wasan ƙarshe na Kofin Mata na Afirka (WAFCON) 2024 da za a fafata ranar Asabar, 26 ga Yuli, 2025. Wannan na zuwa ne yayin da Najeriya ke fatan lashe kofinta na 10 a tarihin gasar.

Najeriya ta riga ta lashe kofin sau tara, kuma ta doke dukkan wasannin karshe da ta buga a baya, sai dai ta gaza samun kofin ne kawai a shekarun 2008, 2012 da 2020.

Google search engine

A bangaren, tawagar mata ta kasar Maroko mai masaukin baki a bana, itama na fatan daukar kofinta na farko, bayan da ta sha kashi a wasan kusa da na karshe a 2022 hannun Najeriya da ci 5-4 a bugun daga kai sai mai tsaron raga.

Super Falcons sun doke Afirka ta Kudu 2-1 a wasan kusa da na ƙarshe, yayin da Maroko ta lallasa Ghana a bugun fenariti 4-2 bayan wasan ya tashi 1-1.

Za a fafata wasan ne a filin Stade Olympique da ke Rabat, kuma dukkanin kasashen biyu sun nuna jajircewa wajen neman nasara a wannan gasa ta mata mafi girma a Afirka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara