Dakarun sojojin Najeriya da ke ƙarƙashin Operation FANSAN YANMA sun kawo kashen fitaccen shugaban ƴan bindiga da aka fi sani da Dan Dari Biyar a wani samame da suka kai a yammacin ƙaramar hukumar Sabon Birni, Jihar Sokoto.
Wata majiya mai karfi daga rundunar sojin ƙasa ta tabbatarwa da Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) cewa an yi ajalin shugaban ƴan ta’addan ne ranar Alhamis a cikin dajin dake tsakanin Turtsawa, Mazau da Zango, lokacin da yake ƙoƙarin karɓar kudin fansa daga iyalan waɗanda suka sace.
Majiyar ta bayyana cewa Dan Dari Biyar yana da mugun hali, inda ke azabtar da waɗanda aka sace kafin ya nemi kuɗi masu yawa.
Rahoton jaridar Daily Nigerian yace an kuma gano makamai, harsasai da na’urorin sadarwa daga wajen harin, yayin da sojoji ke ci gaba da bin sahun ragowar ‘yan ƙungiyar.



