DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ƴan bindiga sun yi ajalin mutane 38 duk da sun karbi Naira miliyan 50 a Zamfara

-

Wasu ƴan bindiga sun yi ajalin mutane 38 daga ƙauyen Banga, karamar hukumar Kauran-Namoda ta jihar Zamfara, duk da cewa an biya su kuɗin fansa fiye da Naira 50 miliyan.

Shugaban karamar hukumar Kauran -Namoda, Mannir Haidara Kaura, ya tabbatar da cewa 56 ne aka sace, amma 18 daga ciki ne kacal suka dawo a raye bayan biyan fansar.

Google search engine

Ya ce an kwantar da waɗanda suka dawo a asibiti domin samun kulawar likitoci, kana gwamnatin jihar tana shirin ziyartar iyalan waɗanda suka rasu sakamakon waki’ar.

Rahoton gidan talabijin na Channels ya ce wani mazaunin ƙauyen, Ibrahim Banga, ya bayyana cewa ƴan bindigar sun nemi Naira miliyan 1 a kan kowanne mutum, amma bayan biyan kuɗin, sai suka kashe sauran 38 cikin zalunci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara