DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Lamarin lantarki na kara munana a sassan Nijeriya in ji wani sabon rahoton jaridar Daily Trust

-

Duk da karin farashin wutar lantarki, al’ummar jihohi da dama a Najeriya na ci gaba da fama da karancin wuta da kuma rashin tabbas a samun ta, musamman a Kano, Borno, Kaduna, Lagos, Ogun, Binuwai da Filato.

Rahotannin da jaridar Daily Trust ta tattaro sun nuna cewa masu masana’antu da ‘yan kasuwa kanana na fuskantar matsin tattalin arziki sakamakon karin farashin Band A, inda ake bukatar a ba su wuta har na sa’o’i 20 a rana, amma ba ta samuwa.

Google search engine

A Kano, masana’antun Sharada da Dakata na korafi kan cewa suna kashe miliyoyi Naira a wata, amma har yanzu sai sun dogara da janareto saboda rashin wadatacciyar wuta.

Masani a fannin sarrafa sharar robobi, Yusuf Bello Yakasai, ya ce yana biyan har Naira miliyan 4 a wata amma har yanzu bai samun ingantacciyar wuta.

A cewar hukumar NERC, kashi 53.2 cikin 100 na masu amfani da wuta a Najeriya ba su da mita, don haka ana ci gaba da karbar kudaden da aka kimanta ba bisa adalci ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara