DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Najeriya na rasa Naira tiriliyan 17.9 a duk shekara saboda cutar hanta – Ministan Lafiya

-

Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa Najeriya na asarar kuɗi tsakanin Naira tiriliyan 13.3 zuwa Naira tiriliyan 17.9 a kowace shekara, saboda cutar hanta da tasirinta na kai tsaye da wanda ba na kai tsaye ba.

Rahoton jaridar Punch ta Ambato ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate, ya bayyana hakan a taron manema labarai na bikin ranar ciwon hanta ta Duniya.

Google search engine

A cewarsa, Najeriya tana ɗaya daga cikin ƙasashen uku mafi yawan masu ɗauke da ciwon hanta a duniya, inda mutane fiye da miliyan 20 ke dauke da cutar, ciki har da miliyan 18.2 da Hepatitis B, da miliyan 2.5 da Hepatitis C.

Ya kara da cewa a kowace shekara, cutar na kashe mutum 4,252 a Najeriya ta hanyar haddasa cancer hanta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara