DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu zai karɓi tawagar Super Falcons a fadar Villa bayan lashe kofin Afirka na mata WAFCON

-

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu zai karɓi ‘yan wasan Super Falcons a fadar Aso Villa, bayan nasarar da suka samu a gasar cin kofin Afirka ta Mata ta 2024 WAPCON.

Super Falcons sun lashe kofin karo na 10 bayan da suka doke ƙasar Morocco mai masaukin baki, a wasan ƙarshe da aka buga a Rabat.

Google search engine

Tuni Gwamnonin Nijeriya; Uba Sani na Kaduna, da AbdulRahman AbdulRazaq na jihar Kwara, da Hope Uzodimma na jihar Imo, tare da ministocin tarayya, sun tarbi tawagar a filin jirgin saman Abuja domin nuna farin ciki da yabo ga nasararsu.

Haka kuma, ‘yan wasan Falcons hudu -Rasheedat Ajibade, Esther Okoronkwo, Michelle Alozie da Chiamaka Nnadozie, sun shiga cikin Best XI na gasar, inda CAF ta bayyana su a matsayin fitattun ‘yan wasa. Ajibade ce aka zaɓa a matsayin Mafi Kyawun ‘Yar Wasa a gasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara