DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun kai hari kayuka 16, sun yi ajalin mutum 5, sun yi garkuwa da wasu da dama a jihar Zamfara

-

‘Yan bindigar da suka kai hari a akalla garuruwa 16 tsakanin Asabar da Lahadi, a ƙaramar hukumar Kaura Namoda ta jihar Zamfara sun yi aja mutane 5 tare da yin garkuwa da mata da dama.

Wani mazaunin yankin ya bayyana cewa a ranar Asabar, ‘yan bindigar sun farmaki garuruwa 8 ciki har da Dan Isa, Kyatawa, Tudu, Gidan Haruna, da sauransu, inda suka kashe mutum 1 a Gidan Haruna kuma suka sace mata 8.

Google search engine

A ranar Lahadi kuma, sun sake dawowa Kwalau inda suka kashe mutum 4 — Abubakar, Murtala, Aminu da Bello — tare da raunata wani Ashafa, wanda aka kai asibitin Kaura Namoda.

Rahotan jaridar Daily Trust ya ce ‘yan sa-kai sun yi musayar wuta da ‘yan bindigar a daren Asabar, lamarin da ya sa suka ja da baya.

Sai dai, da safe sun dawo cikin shiri, inda suka kai farmaki wajen taron ‘yan sa-kai, inda suka kashe 4, suka raunata 1, tare da sace mata da kwashe kayan abinci da na gida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara