Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya gargadi cewa sake zaben Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC a 2027 zai lalata ragowar hadin kai da zaman lafiya a Najeriya.
Da yake jawabi a wani taron jam’iyyar adawa ta ADC a Sokoto, El-Rufai ya ce ba wai yana siyasa don kansa ba ne, sai dai don gyara kura-kuran gwamnati mai ci.
Rahoton jaridar Daily Trust ya malam Nasiru na bayyana cewa gwamnatin yanzu na barazana ga makomar kasa, kuma ya sha alwashin hada kai da sauran ‘yan Najeriya don kawar da APC daga mulki.
El-Rufai ya fice daga jam’iyyar APC a watan Maris 2025 zuwa jam’iyyar SDP, yana mai bayyana rashin jin dadinsa da salon mulkin gwamnatin Tinubu.



