Ministan sufurin jiragen sama kuma jigo a gwamnatin Tinubu, Festus Keyamo, ya bayyana cewa dan takarar adawa Peter Obi ba zai iya samun kuri’u sosai a yankin Arewa ba kamar yadda shugaban kasa Bola Tinubu zai iya yi a zaben 2027.
A wata hira da aka yi da shi a shirin Sunday Politics na Channels Television, Keyamo ya ce jam’iyyar APC da shugaban kasa Tinubu na da goyon bayan siyasa da tsari a Arewa wanda zai ba su damar sake samun nasara.
Ya kuma ce sabon kawancen jam’iyyun adawa da aka kafa karkashin jam’iyyar ADC ba zai je ko ina ba saboda rashin farin jinin su a fadin kasar.


