DCL Hausa Radio
Kaitsaye

INEC ta ja kunnen jam’iyyun siyasa a Nijeriya game da fara yakin neman zabe da wuri

-

Hukumar zaben Nijeriya INEC ta gargadi jam’iyyun siyasa da magoya bayansu da su guji fara yakin neman zabe gabanin zabukan 2027, inda ta bayyana hakan a matsayin karya dokar zabe.

Gargadin na INEC ya zo ne a daidai lokacin da ake samun yawaitar tarukan siyasa a fadin kasar, da sanya allunan hotunan ‘yan takara a allunan talla.

Google search engine

Sakataren yada labaran shugaban hukumar ta INEC, Rotimi Oyekanmi, ya ce har yanzu hukumar ba ta fitar da jadawalin zaben 2027 ba.

Kazalika ba a gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyu ba, kuma babu wata jam’iyyar siyasa da ta fitar da sunayen ‘yan takara a babban zaben mai zuwa ba,yin hakan ya sabawa sashi na 94,(1) na dokar zabe ta 2022.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ƴan Nijeriya sun rage fita kasashen waje neman lafiya karkashin mulkin Tinubu – Rahoton jaridar Punch

Babban bankin Nijeriya, CBN ya bayyana cewa ’yan Nijeriya sun kashe dala miliyan 4.74 wajen neman lafiya a kasashen waje daga Mayu 2023 zuwa Maris...

Jam’iyyar PDP reshen Arewa maso Yamma ta nesanta kanta da Tanimu Turaki a matsayin dan takarar shugabancin jam’iyyar daga yankin

Jiga-jigan jam’iyyar PDP daga yankin Arewa maso Yamma sun nesanta kansu daga amincewar da aka yi da tsohon ministan ayyuka na musamman, Tanimu Turaki, SAN,...

Mafi Shahara