DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bangladesh ta mayar wa alhazan 2025 rarar sama da Naira dubu 500

-

Ma’aikatar Harkokin Addini ta Bangladesh ta mayar da Taka dubu 46,725 ga kowane mahajjacin bana, bayan rage kuɗin masauki a Saudiyya.

Jimillar kuɗin da aka mayar ta kai Taka miliyan 82, wanda ya yi daidai da sama da Naira dubu 500 ga kowane mahajjaci.

Google search engine

Mai ba da shawara kan harkokin addini, AFM Khalid Hossain, ya ce wannan nasarar ta biyo bayan bin dokokin Saudiyya da kuma biyan kuɗin Hajj akan lokaci.

A bana, mahajjata 87,100 daga Bangladesh ne suka halarci Hajj, inda kuɗin shirin ya ragu da Taka 73,000 ga kowane mutum idan aka kwatanta da bara.

Sun kuma samu masauki kusa da Ka’aba tare da sabbin hidimomi kamar manhajar Labbike, layin waya, da katin biyan kuɗi na Hajj.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara