DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Har yanzu ba mu samu dala $100,000 da gidajen da Tinubu ya yi mana alkawari ba – Ajibade

-

Kyaftin din kungiyar Super Falcons, Rasheedat Ajibade, ta bayyana cewa gwamnatin tarayya har yanzu ba ta cika alkawarin da Shugaba Bola Tinubu ya yi wa tawagar ba, bayan nasarar da suka samu a gasar cin kofin zakarun Afrika na 2025 WAFCON da aka yi a Maroko.

A wata hira da ta yi da jaridar Guardian, Ajibade ta tabbatar cewa ba su samu dala $100,000 ba kuma ba a mika musu sauran kyaututtukan da aka yi alkawari ba, ciki har da gidaje.

Google search engine

Sai dai ta ce duk da haka, ’yan wasan na da kyakkyawan fata cewa gwamnati za ta aiwatar da alkawarin da ta dauka musu.

Ajibade wacce aka zaba a matsayin ‘yar wasan da ta fi kowa kwazo, ta jagoranci kungiyar zuwa lashe kofin WAFCON karo na goma wanda babu irinsa a tarihi a nahiyar.

1 COMMENT

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara