DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa miliyan 20 daga yanzu zuwa shekarar 2030

-

Gwamnatin tarayyar Nijeriya ta kaddamar da shirin horas da matasa da nufin samarwa matasa miliyan 20 damar samun aiki da hanyoyin kasuwanci daga yanzu zuwa shekarar 2030.

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ne ya sanar da hakan a taron farko na kwamitin gudanarwa na Generation Unlimited Nigeria da aka gudanar a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Google search engine

Shettima, wanda shi ne shugaban kwamitin, ya bayyana cewa akalla kashi 60 na wadanda zasu amfana da shirin mata ne.

Ya ce tsarin ƙwarewar sana’o’in matasa a ƙasar na fuskantar manyan ƙalubale kashi uku kuma matasa da dama ba sa samun damar shiga shirye-shiryen domin samun horo.

Ya kuma ce babu isassun kayan aiki da za su basu damar samun horon cikin sauki.

2 COMMENTS

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara