DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ana fargabar mutane 30 sun hadu da ajalinsu a lokacin da kwale-kwale ya kife da su cikin kogi a jihar Sokoto

-

Hukumar bada agajin gaggawa ta Kasa NEMA, tace har yanzu tanaci gaba da aikin ceton mutane bayan kifewar wani jirgin ruwa a jihar Sokoto da yayi sanadiyyar batan gwamman mutane.

A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar ta bayyana cewa, jirgin wanda ke dauke da fasinjoji sama da 50 da ke a kan hanyarsu ta zuwa kasuwa ya kife ne da safiyar Lahadi.

Hukumar tace a halin yanzu Mutane 10 ne aka iya cetowa, yayin wasu da dama kuma sukai batan dabo da har yanzu ake ci gaba da nemansu.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An gudanar da addu’o’in neman tsari daga hare-haren ‘yan bindiga a jihar Neja

Mazauna yankin jihar Neja ta Arewa sun gudanar da addu’o’i na musamman a filin Idi da ke Kontagora, hedkwatar karamar hukumar Kontagora, domin neman taimakon...

‘Yan siyasa a Nijeriya sun fi maida hanakali kan siyasa maimakon magance matsalolin al’umma – Sarkin Onitsha

Sarkin Onitsha, Igwe Nnaemeka Achebe, ya caccaki ‘yan siyasa bisa mayar da hankali kan siyasa maimakon gudanar da mulki yadda ya kamata tun kafin zaben...

Mafi Shahara