Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana shirin ta na ɗaukar nauyin auren wasu matasa da suka ajiye makamai tare da yin alkawarin barin ayyukan daba da tashin hankali.
Kwamandan hukumar Hisbah, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa, ne ya bayyana haka bayan sama da matasa 1,000 sun ajiye makaman su tare da rungumar zaman lafiya.
Sheikh Daurawa ya ce wannan shiri na daga cikin manufofin Gwamna Abba Kabir Yusuf, wajen ba da damar gyara rayuwa da inganta makomar matasa da ke aikata laifi.
Ya gargade su da su zama mutane na gari tare da kira da sauran da ke irin wannan dabi’a su dawo domin rungumar zaman lafiya.
An gudanar da taron ne a Hedikwatar hukumar ‘yan sandan jihar Kano da ke Bompai,tare da sauran jami’an tsaro da masu ruwa da tsaki.



