Kungiyoyin al’umma a ƙarƙashin League of Civil Society Organisations a jihar Kano sun bukaci gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta ɗauki matakin gaggawa kan zargin rashawa da ake yi wa wasu manyan jami’an gwamnati.
Kungiyoyin sun bayyana cewa lamarin ya nuna mummunan tsarin cin hanci da wofantar da amana, wanda zai iya tasiri wajen korar masu sha’awar zuba jari a jihar.
Sun ce binciken ICPC da EFCC ya gano badakala guda biyu, ciki har da na shugaban hukumar zaɓe ta Kano (KANSIEC), Sani Malumfashi, tare da sakataren hukumar Anas Mustapha da wani mataimakin darakta a sashen kuɗi.
Rahoton ya nuna sama da N1bn aka karkatar daga asusun hukumar a Unity Bank, inda aka mayar da shi zuwa wani kamfani na kashin kai da sunan biyan ma’aikatan wucin gadi, duk da cewa an riga an biya su ta banki.
Jaridar Premium Times ta ruwaito cewa kungiyoyin sun yi gargadin cewa rashin ɗaukar mataki mai ƙarfi daga gwamnati kan iya lalata amincewar jama’a da kuma kawo cikas ga ci gaban Kano.



