DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dan takara mara nagarta na iya rusa haɗin kan jam’iyyun adawa a 2027 – Sule Lamido

-

Tsohon gwamnan jihar Jigawa kuma jigo a jam’iyyar PDP, Alhaji Sule Lamido, ya ce makomar haɗin kan jam’iyyun adawa a zaben 2027 za ta dogara ne kan wanda za a zaɓa a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa.

Lamido ya bayyana haka ne a wata hira da ya yi da Daily Trust, inda ya yi tsokaci kan rade-radin yiwuwar haɗa kai da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan, makomar jam’iyyar PDP da kuma dalilin da ya sa yake ganin zaɓen ɗan takara da bai dace ba zai iya raunana ƙarfin haɗin kan jam’iyyun adawa.

Google search engine

Da aka tambaye shi game da rade-radin cewa tsohon shugaban ƙasa Olusegun Obasanjo ya zaɓe shi a matsayin mataimakin Jonathan a zaben 2027, Lamido ya ce labarin abin dariya ne.

Sai dai rahoton Daily Trust ya ruwaito shi yana gode wa al’ummar Najeriya da suke ganin daraja da cancantarsa, yana mai cewa ya yi mamaki da irin kallon da ake masa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara