DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Magoya bayan APC masu tarin yawa sun fice sun koma ADC a jihar Sokoto

-

Wasu tarin magoya bayan jam’iyyar APC a karamar hukumar Gada ta jihar Sokoto sun fice daga jam’iyyar tare da komawa jam’iyyar ADC, inda suka danganta hakan da rashin gamsuwa da yadda jam’iyyar mai mulki ke gudanar da al’amuranta a jihar.

An karɓi waɗanda suka sauya sheƙar ne a hukumance daga hannun Sanata Abubakar Gada, wanda ya bayyana wannan ci gaban a matsayin wani ɓangare na ƙoƙarin kafa haɗin gwiwa mai faɗi domin ceto jihar Sokoto da kasa baki ɗaya daga abin da ya kira gazawar mulki.

Google search engine

Da yake jawabi a wajen taron tarbar sababbin mambobin, Sanata Gada ya ce yawan rashin jin daɗi da jagorancin APC ya sanya mutane da dama shiga jam’iyyar ADC domin neman samun sauyi mai ma’ana.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara