DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akpabio ya roƙi ‘yan Najeriya su rika kare aikace-aikacen gwamnati

-

Shugaban majalisar dattawan Nijeriya, Sanata Godswill Akpabio, ya shawarci al’ummomi su kiyaye da kuma kula da ayyukan da gwamnati ke shimfiɗawa a yankunansu.

Ya bayyana haka ne a lokacin da ya kaddamar da wasu ayyuka a karamar hukumar Ika ta jihar Akwa Ibom.

Google search engine

Jaridar Punch ta ruwaito Akpabio ya ce jama’a su ɗauki wadannan ayyuka a matsayin mallakinsu, domin idan aka lalata su, to an cutar da al’umma gaba ɗaya.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin Shugaba Bola Tinubu na da niyyar kawo sauƙi ga talakawa ta hanyar samar da tallafi da ingantattun ayyuka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara