Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya sauke dukkanin kwamishinoninsa, tare da umartar manyan sakatarorin ma’aikatun jihar da su ci gaba da rike ragamar ma’aikatun har zuwa lokacin da za a nada sababbin kwamishinoni.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a Litinin din nan yayin taron majalisar zartarwa, inda ya yi gargaɗi ga tsoffin kwamishinonin da kada su yi yunƙurin neman taimako ko shiga sahun masu neman mukaman gwamnati.
Ya ce cikin mako guda zuwa biyu zai sanar da sabuwar majalisar zartarwa, inda ya bayyana cewa ya riga ya yi nazari kan ayyukan kowanne daga cikin tsoffin kwamishinonin.
A cewarsa, akwai wadanda suka taka rawar gani a ayyukansu, yayin da wasu kuma ba su samu damar yin ayyukan da aka dorasu akai ba.



