Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatin sa ba za ta nuna bambanci ba, wajen samar da ababen more rayuwa da ayyukan ci gaba ga yan kasa.
Tinubu ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa da ya fitar, inda ya jaddada cewa rantsuwar da ya dauka ita ce yi wa dukkan ’yan kasa hidima ba tare da nuna bambancin siyasa ko yanki ba.
Ya lissafa manyan ayyuka kamar titin Lagos–Calabar, Sokoto–Badagry Superhighway, layin dogon Port Harcourt–Maiduguri, da hanyar Abuja–Kaduna–Kano a matsayin shaida cewa babu wani yanki da ake watsi da shi.
Shugaban ya kuma bayyana cewa gwamnati na samar da ayyukan yi ga sama da mutane 250,000, gyaran cibiyoyin lafiya a fadin Nijeriya, tare da dawo da wutar lantarki a Kaduna ta hanyar sabunta injinan samar da wuta mai karfin megawatts 255.



