Jam’iyyar ADC ta bayyana cewa babu wani umarnin kotu da aka bayar a kan sabon shugaban jam’iyyar na kasa, Sanata David Mark, da sakataren jam’iyyar na kasa, Tsohon Ministan Harkokin Cikin Gida, Rauf Aregbesola.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa magana da yawun jam’iyyar na kasa, Bola Abdullahi, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa a ranar Alhamis, inda ya ce bayan gazawar wasu masu son zuciya wajen hana INEC amincewar da sabon shugabancin jam’iyyar, yanzu sun koma yada labaran karya.
ADC, wacce ke kan gaba cikin jam’iyyun adawa a Najeriya, ta shiga rikicin shugabanci a ‘yan watannin nan, lamarin da ya kara kamari bayan hukumar INEC ta tabbatar da sabon shugabancin jam’iyyar karkashin David Mark a matsayin shugabanta na kasa da kuma Rauf Aregbesola a matsayin Sakataren Kasa.



