DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ghana ta fara karbar ‘yan kasashen yammacin Afirka da Amurka ta koro

-

Shugaban ƙasar Ghana, John Dramani Mahama, ya tabbatar da cewa ƙasarsa ta fara karɓar wasu ‘yan ƙasashen Yammacin Afirka da Amurka ta koro, ciki har da ‘yan Nijeriya.

Mahama ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin da yake zantawa da manema labarai, inda ya ce wannan mataki ya biyo bayan wata yarjejeniya ta diflomasiyya da aka kulla.

Google search engine

Shugaban ya ƙara da cewa matakin ya shafi ƙasashen yammacin Afirka daban-daban, kuma Ghana za ta yi aiki tare da hukumomin ƙasashen da abin ya shafa domin tabbatar da cewa an dawo da waɗanda aka koro cikin mutunci da tsari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara