DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kebbi Nasir Idris ya dakatar da Kwamishinan Lafiya saboda sakaci a bakin aiki

-

Gwamnan jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin dakatar da Kwamishinan Lafiya na jihar, Kwamared Yunusa Isma’il, daga mukaminsa nan take har zuwa wani lokaci.

Sanarwar da Sakataren Gwamnatin Jihar, Alhaji Yakubu Bala Tafida, ya fitar a yau Alhamis a Birnin Kebbi, ta bayyana cewa an ɗauki wannan mataki ne bisa zargin sakaci da yin watsi da aikinsa.

A cewar sanarwar, Gwamna Idris ya umarci Kwamishinan da aka dakatar ya bayar da cikakken bayani kan dalilin da zai sa kada a ɗauki matakin ladabtarwa a kansa.

Hakan, a cewar gwamnatin jihar, ya biyo bayan raina aikinsa da kuma rashin mutunta amanar da aka ɗora masa a matsayin Kwamishinan Lafiya.

Google search engine
Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara