DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar NUPENG ta yi barazanar komawa yajin aiki

-

Rahoton gidan talabijin na Channels ya nuna cewa, kwana biyu kacal da kungiyar masu dakon man fetur da iskar gas ta Najeriya (NUPENG) ta dakatar da yajin aikin ta, kungiyar ta sake Zargin hukumar kamfanin Dangote Refinery da karya yarjejeniyar da aka cimma.

A cikin wata sanarwa da Shugaban NUPENG, Williams Akporeha, tare da Sakataren Janar, Afolabi Olawale suka rattaba wa hannu, kungiyar ta gargadi cewa za ta iya sake komawa yajin aikin da aka dakatar, saboda karya matsayar da aka cimma tsakanin Dangote Refinery, gwamnatin tarayya da direbobin manyan motoci da ke karkashin kungiyar NUPENG-PTD.

Google search engine

Sai dai duk da wannan matsayi da aka rattaba hannu a ofishin DSS, a jiya an umarci direbobin manyan motoci da ke cikin NUPENG-PTD da su cire tambarin kungiyar daga motocinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara